Majalisar Kolin Alkalan Nijeriya, wato NJC ta zabi mutane hudu da ke son a nada a matsayin sabbin Alkalai a kotun koli.
Sanarwar neman nadin ta fito ne daga bakin Daraktan yada labarai na NJC, Soji Oye, ESQ a ranar Alhamis 24 ga watan Oktoban 2019. Wadanda aka za a yi wa nadin su ne:
1. Hon. Justice Adamu Jauro (Yankin Arewa maso Gabas)
2. Hon. Justice Emmanuel A. Agim
(Yankin Kudu maso Kudu)
3. Hon Justice C. Oseji, JCA (Yankin Kudu maso Kudu)
4. Hon Justice Helen M. Ogunwumiju, (Yankin Kudu maso Yamma)
Har ila yau, NJC ta kuma bukaci a nada wasu jami’an ma’aikatan shari’ar 13 a manyan kotunan tarayya da jihohi kamar yadda ya ke cikin sanarwar ta majalisar ta fitar.
Alkalan sun fito ne daga sassan Nijeriya daban-daban kuma za a nada wasu daga cikinsu a matsayin Alkalan kotu nan tarayya yayin da wasu kuma alkalan kotunan jihohi.
Ana sa ran dukkan za a rantsar da dukkan Alkalan da aka zaba bayan Shugaban kasa da Gwamnonin jihohinsu da Majalisar Dattawa da ta jihohi sun amince da su.