Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC reshen jihar Legas ta bayar da wa’adin makonni biyu ga gwamnatin tarayya da ta kawo karshen yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ASUU ta fara.
Da take jawabi a wajen zanga-zangar a Ikeja, shugabar kungiyar NLC ta Legas, Misis Agnes Sessy, ta bukaci gwamnati da ta dauki mataki ko kuma a fuskanci tsaiko daga bangarori da dama.
DUBA WANNAN LABARIN: Rundunar Soji ta musanta garkuwa da jami’anta
Kungiyar NLC da sauran kungiyoyin jami’o’i sun fito kan titunan Legas domin nuna rashin amincewarsu da yajin aikin ASUU wanda aka gudanar ranar Talata.
Ta ce: “Idan har gwamnatin tarayya ba ta warware yajin aikin cikin makonni biyu ba, za a yi zanga-zanga a fadin kasar.
A zahiri, zanga-zangar ENDSARS za ta zama wasan yara akan wadda zamuyi.” inji ta.
Reshen kungiyar Kwadagon na jihohin kasar nan baki daya ne, suka gudanar da Zanga zangar A jihohin su.