Hukumar NYSC ta karyata labarin da ke yawo kan cewa an kara wa ‘yan bautar kasa kudin alawus din da ake basu daga dubu 19,800 zuwa 31,800. Mataimakin Darakta na hukumar, Eddy Megwa ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar Laraba, inda ya ce, har yanzu Gwamnatin tarayya ba ta sanar da hukumar tasu komai kan karin alawus din ba. Ya kara da cewa, duk da yake Gwamnatin tarayya ce ke biyan ma su hidimar kasar kai tsaye, to amman Gwamnatin tarayyar za ta sanar da hukumar idan har ta kara alawus din. “Duk wani kudi da ake biyan ‘yan bautar kasaba hukumar NYSC ce ke biyan su ba, Gwamnatin tarayya ce ke biyansu kai tsaye. Ba za mu iya fadar magana kan karin alawus din ma su hidimar kasa ba, har sai abin da Gwamnati ta yi dangane da karin mafi karancin albashi,” in ji shi. Mataimakin Daraktan ya yi kira da cewa, “Kar ku yarda da duk wani labarin karin alawus da ke yawo a soshiyal midiya. Duk Lokacin da Gwamnatin tarayya ta shirya yin karin, za ta sanar da mu, a nan mu kuma, sai mu sanar da ‘yan bautar kasata sahihin adireshin mu.”