By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Anambra, Cif Willie Obiano, ya ayyana ranakun Alhamis da Juma’a amatsayin ranar hutu inda yace babu ayyukan yi domin baiwa mazauna jihar damar shirya zaben gwamna da za’ayi a ranar Asabar mai cike da lumana.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ma’aikata ta shekarar 2021 da aka gudanar a dakin taro na Jerome Udeorji, dake Awka, babban birnin jihar a ranar Laraba.
Obiano yace, “Hukuncin jama’a shi ne don baiwa ma’aikatan jihar damar shirya kansu domin zaben gwamna da za a yi ranar Asabar. Ina kira ga ma’aikata dasu hada kan makwabtansu domin dole ne a yi zabe.
“Ina yaba wa ma’aikatan jihar bisa hadin kan da suke baiwa gwamnatina. Na cika musu alkawuran da na yi musu, na kuma kara karawa”.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa gwamnan ya kara jaddada muradinsa na ganin Farfesa Chukwuemeka Soludo ya gaje shi, ya kuma bukaci ma’aikata da mazauna yankin dasu zabe shi, yana mai jaddada goyon bayansa ga Soludo saboda asalinsa ne.
Comments 2