Wakilinmu Mohammed Gambo
Ofishin Mataimakin shugaban kasa yace bai sa Ido kan kirkiro da mazaunun makiyaya da akai ma Lakabi da (Ruga Settlements) kamar yadda wasu kafafen yada labarai ke yadawa ba.
Laolu Akande, wanda shine mai tallafawa Mataimakin shugaban kasa a fannin sadarwa yace ofishin Mataimakin shugaban kasan ya musanta rahoton da yayi magana akan hakan wanda aka fitar ranar juma’a a birnin Abuja.
Mazaunun da ake kira Ruga settlements ya ban-banta da shirin bunkasa kiwo na kasa wanda gwamnonin jihohi suka amince dashi a karkashin Majalisar lura da tattalin arzikin kasa(NEC) wanda Mataimakin shugaban kasa Yemi Osibanjo yake shugabanta.
Akande yace NEC, ta amince da shirin ranar 17 ga watan Janairu bisa shawarwarin kwamitin kwararru na Majalisar, karkashin jagorancin Gwamnan jihar Ebonyi Dave Umahi.
Yace wasu gwamnonin jihohin dake cikin kwamitin da bangarorin dake aiki a karkashin NEC din sun hada da Gwamnan jihar Adamawa, na Kaduna, Benue, Taraba, Edo, Plateau, da na jihar Zamfara wadan da mafi yawan su ke fama da rikicin manoma da makiyaya.
“Shirin bunkasa kiwo na kasa wato (NLTP) na shekara ta 2019 zuwa shekara ta 2028, shiri ne da ake da niyyar kaddamar dashi a jihohi bakwai kamar jihar Adamawa, Benue, Kaduna, Plateau, Nasarawa, Taraba da jihar Zamfara kamar yadda NEC, ta amince da shi a Janairu.
Bayan nan kuma jihohi shida da suka hada da jihar Katisna, Kano, Kogi, Kwara Ondo, da Edo, suma suka nuna bukatar su na kaddamar da shirin.
Shirin na da matsaya shida wadan da ta hanyar su ne zai bunkasa kiwo a Nijeriya a bangaren kasuwanci da kuma shimfida yanayin da zai kawo zaman lafiya da adalci.
Matsaya shidan kuwa sune:-
– Saka hannu jari ga tattalin arziki.
– Sasanta rashin jituwa.
– Adalci da zaman lafiya.
– Tallafi
– Agajin gaggawa.
– Da kuma karfafa al’umma domin cigaba.
Sauran sun hada da la’akari da al’amura kamar abubuwan da suka shafi jinsi, Matasa, bincike da yada labarai da dai sauransu
Yace Gwamnatin tarayya ba zata tirsasawa wata gwamnatin jiha akan hakan ba.