Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu mutane hudu da suka hada da wani basaraken gargajiya a Ikare Akoko, Babban Cif Mukaila Bello a yammacin ranar Alhamis din nan yayin da suke kan hanyar daga Akure, babban birnin jihar zuwa Ikare-Akoko.
An bayyana cewa lamarin ya faru ne a Ago Yeye axis, daura da titin Owo/Ikare.
Direban motar da ke dauke da su an ce harsashin maharan ya same shi a kai kuma yanzu haka yana karbar magani a wani asibiti da ba a bayyana ba a garin Owo.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Ondo SP Funmilayo Odunlami ta tabbatar da faruwar lamarin.
KARANTA WANNAN: https://dimokuradiyya.com.ng/kogi-wasu-yan-bindiga-sun-yi-garkuwa-da-yara-uku-sun-nemi-kudin-fansa/
Ta bayyana cewa an gano motar, wata mota kirar Toyota Corolla mai lamba KAK 818 AE yayin da direban ke karbar magani a wani asibiti da ke kusa.
Odunlami ta kara da cewa, an aike da tawagar ‘yan sanda zuwa yankin inda suka rike sintiri a daji da ke kusa da su domin kamo masu garkuwa da mutanen da kuma ceto wadanda lamarin ya shafa.
(CHANNELS TV)