- Hakalin Gwamnatin jihar Abia ya tashi da har yanzu wasu jami’an gwamnatin da ta shude suke cigaba da rike kadarorin gwamnati.
- Gwamnati ta umurci duk wanda ke da kadarorin a wajensa da ya mayar da su zuwa ofishin SSG a ranar Talata, 6 ga watan Yuni, 2023,
- Rashin bin wannan umarnin zai jawo kakaba takunkumi.
Gwamnatin jihar Abia ta ce hankalinta ya yi matukar tashi cewa har yanzu wasu jami’an gwamnatin da ta shude a jihar suna rike da kadarorin gwamnati,Daily Post ta rawaito.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Kenneth Kalu, a ranar Lahadi, ya ce kadarorin gwamnati sun hada da motoci, janareta, kwamfutocin tafi da gidanka da sauransu.
KARANTA WANNAN: Abubuwa Biyar Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cire Tallafin Man Fetur
Gwamnati ta umurci duk wanda ke da kadarorin a wajensa da ya mayar da irin wannan zuwa ofishin SSG da karfe 4 na yamma a ranar Talata, 6 ga watan Yuni, 2023, sannan ya sami takardar shaidar da ta dace daga ofishin.
Sanarwar ta kara da cewa “Don Allah a lura cewa rashin bin wannan umarnin zai jawo kakaba takunkumi.”
A wani labarin kuma, Gwamnati Mai Ci Ta Wucin Gadi Ce, Zan Karbo Kujerata A Kotu – Atiku Ga Tinubu
Atiku Abubakar, ya bayyana gwamnati mai ci ta shugaba Bola Tinubu a matsayin ta wucin gadi.
Atiku ya jaddada cewa zai karbo kujerarsa da aka sace a kotu.
Ya bayyana hakan ne a yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP na zababbun jami’an jam’iyyar a Bauchi ranar Asabar.