Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar Labour Party, LP, Peter Obi, ya ce ba zai yi watsi da Najeriya ba idan Yaƙi ya Ɓarke a Ƙasar.
Obi ya ce ya Gwammace ya mutu a Najeriya idan yaƙi ya ɓarke da ya zama mai ƴanci a wata ƙasa.
Ya bayyana hakan ne a yayin wani zaman tattaunawa da ya yi da mambobi sama da 1,000 na Babbar Ƙungiyarsa ta goyon bayan sa wato Peter Obi Support Network.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan Jam’iyar PDP Sama Da 2,500 Sun Koma APC A Jihar Kebbi
Tsohon Gwamnan Jihar Anambra ya ce da gangan ya kaucewa samun takardar izinin zama ɗan kasa a wasu ƙasashe saboda ya yi imani da Najeriya.
A cewar Obi: “Lokacin da na bar Burtaniya bayan da na zauna a can sama da shekaru 10, na mayar da duk abin da yake nasu.
“Ina mai da hankali kan Najeriya kacokan, kuma bana tunanin ina buƙatar zama na wata ƙasa idan ban gama amfani da haƙƙi da gata da aka bani ba a matsayina na ɗan Najeriya.
“Idan ba na Najeriya a yau kuma aka yi yaƙi a Najeriya, zan nemo hanyar komawa Najeriya domin in mutu a ƙasata Najeriya da in rayu cikin ƴanci a kasar wani.”
Dan Takarar Shugaban Ƙasar ya yi kira ga ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje da su bayar da tasu gudunmawar wajen ci gaban ƙasar.