Sakamakon gabatowar karshen shekara da ya kasance ana gabatar da bukukuwa kala kala daga kabilu daban daban, yanzu haka an fara samun dogayen layuka a gidajen siyar da man Fetur dake sassan jihar.
Wakilin Jaridar Dimokuraɗiyya ya zagaya wasu tituna a jihar da suka hadar da:
- Titin jami’ar Bayero Kano
- Titin Murtala Muhammad
- Titin Goron dutse
- Titin Muhammadu Buhari
- Titin Sharada Ja’en
- Titin Gwarzo
- Titin zuwa Hadejia
- Titin Hotoro
Abun mamakin da ya tarar shine yadda yawancin gidajen man kan wadannan tituna suka kasance a garkame.
Yayin da wasu kadan daga cikin su, suka kasance a bude, to sai dai tarin abubuwan hawa da suka hadar babura da motoci suka mamaye gidajen man, wanda hakan ya sanya dogayen layuka.
Jaridar Dimokuraɗiyya ta samu zantawa da wasu mutanen da suka je domin siyan man fetur din, inda suka bayyana cewa kusan kwana 4 da suka gabata aka fara samun wannan matsala.
KARANTA WANNAN LABARIN: An kaddamar da tsarin sadarwa na zamani a jihar Kano
To sai dai wasu daga cikin mutanen sun bayyana cewa hakan baya rasa nasaba da yadda karshen shekara ke kara gabatowa.
Wakilin namu yayi kokarin ji daga ɓangaren mahukunta domin jin daga inda matsalar take, amma hakan ya gaza samuwa.
Comments 1