Kungiyar Izalatil Bid’ah Wa’Ikamatis Sunnah (JIBWIS) mai hedikwata a Jos ta tura malamai 533 wuraren da za su gudanar tafsiri Alkur’ani mai girma daban-daban ciki da wajen Najeriya a watan Azumin Ramadan din wannan shekara ta 2019. Shugaban Majalisar malamai na kungiyar na kasa, Shiekh Muhammad Sani Yahaya Jingir, ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke kaddamar da bude tafsirin kungiyar, don tarbar watan Ramadan mai alfarma a masallacin Marigayi Alhaji Sulen Jabu da ke Layin Zana Jos babban birnin jihar Filato da yammacin ranar Juma’ar da ta gabata, inda ya hori malaman da su guji yin sukan tokororinsu malamai a lokacin da su ke gudanar da tafsiransu kuma ya hore su da su tabbata sun isar da sakon Allah (SWA) kamar yadda ya ke a rubuce a cikn Alkur’ani mai girma. Shiekh Jingir haka nan kuma ya ja hankalin ’yan kasuwar kasar nan dasu guji sawwala wa ka yan da suke sayarwa kudi don ganin bukatarsu na karuwa daga wajen masu saye, yace mai makon kara wa kayan da suke sayarwa kudi kamata ya yi su rege faracinsu don samu lada da falalar wannan wata. Ya yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga masu garkuwa da mutane suna nemanfansa da suyi gaggawa su tuba domin yace kofofin tuba abude suke idan suka tuba suka dai na Allah zai karbi tubarsu ya yafemasu kuma ya gargadesu dasu guji kai mutane makura. Shiekh Jingir wanda ya fara karatunsa a aya ta 99 cikin suratul Kahf ya hori al’ummar musulmi da ako yauce su kadaita Allah da ibada kuma su rika aikata ayyukan da Allah ya yi umurni wa bayinsa su aikata kamar taimakawa maras karfi a sakaninsu musamman yace a wannan wata na azumi da ake ninka lada wa mai aikatasu kuma suyi nesa da aikata ayyukan tsabo wadan da Allah ya haramta wa bayinsa da aikatawa kuma ya nemi musulmai da su yi amfani da wannan lokaci don kara yin addu’o’I, wa Allah ya kawo sauki a cikin lamarin rashin tsaro da kasar nan yanzu yake fuskanta.