Ma’aikatan Nijeriya sun bukaci da a hanzarta biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 30,000, kamar yanda Shugaba Buhari ya bayyana a lokacin da ya ke sanya hanna a kan sabuwar dokar. Sun yi kiran ne a wajen bukukuwan ranar ma’aikata da a ka yi a dandalin Eagle Skuare da ke Abuja, inda shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Ayuba Wabba, da shugaban kungiyar ’yan kasuwa ta TUC, Bobboi Bala Kaigama, ne su ka karanta jawabin taron ga ma’aikatan kasar nan. “Ba wata kyauta a wannan ranar kamar ta Naira 30,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi. Mun yabawa Majalisun Tarayya da Shugaba Buhari, a bisa amsawan da suka yi wa bukatar mu ta yin karin a kan mafi karancin albashin, sai dai, ana yin jinkirin aiwatar da shi, ba kamar yanda shugaba Buhari ya yi umurni ba a ranar da yake sanya hannu a kan dokar, kamata ya yi duk masu daukan ma’aikata su hanzarta fara biyan sabon mafi karancin albashin,” in ji su. Ma’aiakatan su ka ce, a sabanin kididdigan da babban bankin kasa ya fitar na cewa, tashin farashin kayayyaki ya ragu da kashi 11.44 a watan Disamba, 2018 zuwa kashi 11.25, amma a gaskiya irin wahalar da ma’aikata da sauran al’umma suke fama da ita, sam wannan bai yi tasiri ba. Su ka ce, iyalan ma’aikatan kasar nan da kyar suke rarrafawa saboda tsadar rayuwa, musamman a fannin abinci da wurin zama mai kyau. Kungiyoyin kwadagon suka yi kira ga shugaba Buhari, da ya kirkiro ayyukan yi masu yawa ta hanyar fadada hanyoyin samar da kudin shiga na tattalin arzikin kasar nan, hakan ya tafi tare da mayar da himma wajen samar da ma’aikatu da masana’antu. Dangane da batun farfado da masakun kasar nan, ma’aikatan sun bukaci da a farfado da kimar samar da Auduga, a kuma sake bin diddigin kudaden nan da aka ware domin farfado da masakun kasar nan. ma’aikatan sun bukaci da a binciki Naira bilyan 100 da aka ware na tallafi a masakun kasar nan a zamanin gwamnatocin tsohon shugaba Obasanjo da kuma Umaru Musa ‘Yar’aduwa.