Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci da a bai wa masu binciken zargin rashawar da ake yi a hukumar NDDC. Shugaba Buhari ya ce akwai bukatar a samu hadin kai a binciken da ake gudanarwa a hukumar lura da ci gaban yankin Neja Delta, NDDC wanda hukumomin bincike ke yi tare da hadin guiwar majalisar kasa.
Hakan ya fito ne a cikin sanarwar da Kakakin shugaban kasar, Malam Garba Shehu ya fitar, inda ya jaddada cewa; shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a lokacin da yake maida jawabi bisa rikicin da yake faruwa tsakanin wadansu mutane a hukumar ta NDDC.
Shugaba Buhari ya ce wadanda za su yi binciken su tabbata sun tsaftace binciken na su fitar da gaskiya a yunkurin da gwamnatinsa ke yi wajen bunkasa yankin na Neja Delta din.
Shugaba Buhari ya yi alkawarin bincikar hakikanin abin da ya faru domin gano musabbabin kitimurmurar da ake kullawa dakile ci gaban yankin na Neja da al’ummar yankin.