By Abbas Yakubu Yaura
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya koka kan yadda yara kimanin 152, 243 ‘yan kasa da shekaru biyar a jihar Enugu ke fama da matsalar ci gaban girman jiki.
Kwararriyar tsare-tsare da sa ido,ta UNICEF da ofishin ta ke jihar Enugu, Misis Maureen Zubie-Okolo ta bayyana hakan a ranar Alhamis, a Enugu, yayin wata tattaunawa ta siyasa tare da majalisun zartarwa da na majalisar dokoki na jihar Enugu kan zuba jari a cikin harkokin abinci.
Zubie-Okolo ta ce rashin abinci mai gina jiki ya taso ne daga rashin ciyarwar mata masu juna biyu, jarirai da kananan yara a cikin kwanaki 1000 na farkon rayuwar yaron.
“A jihar Enugu, kashi 7.8 cikin 100 na yara ‘yan kasa da shekara biyar ne kawai ke samun mafi karancin abincin da za a iya karba yayin da kasa da kashi daya bisa biyar na watanni 0-5 ke shayar da nono kadai.
“Wannan kira ne ga bangarorin zartaswa da na majalisar dokoki na gwamnatin jihar dasu hada kai don tabbatar da cewa an sanya abinci mai gina jiki a cikin ajandar kasafin kudi,” in ji ta.
Sannan ta ce rashin abinci mai gina jiki ya zama abin gaggawa kuma ta koka da cewa duk da rashin jin dadin ci gaban da ake samu ko kadan ba a kula da shi.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Misis Zubie-Okolo tace taron ya yi daidai da ajandar ci gaba mai dorewa na kawo karshen duk wani nau’i na rashin abinci mai gina jiki nan da shekarar 2030, ta kara da cewa, manufar ta kuma hada da cimma manufofin da kasashen duniya suka amince da su na tsugunar da yara ‘yan kasa da shekaru biyar nan da shekarar 2025.
Da yake mayar da martani, kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Enugu, David Ugwunta, yace gwamnatin jihar za ta tattara dukkan batutuwan da aka tattauna a taron tare da halartar su.