Sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma, wato Alhaji Lawali Hassan, ya raba wa mata 1, 200 da naira dubu 10 domin ganin sun fara karamar sana’o’i.
Hajiya Hussaina Uzairu, Shugaban shirin bai wa mata tallafin ta ‘Daniya Women empowerment,’ ita ce ta bayyana hakan a wurin kaddamar da shirin bayar da tallafin a ranar Asabar a garin Bakura wato Hedikwatar karamar hukumar Bakura a jihar.
Hajiya Hussanina Uzairu ta ce mata 200 daga kowanne kananan hukumomi 6 sune za su amfana da tallafin.
Dukkan kananan hukumomi shida din suna karkashin yankin Zamfara ta yamma ne, kuma sun hada da; Anka, Bakura, Bukkuyum, Gummi, Maradun da Talata Mafara.
Ta ce an bai wa kowacce mace naira dubu 10 domin ba ta damar fara gudanar da kananan sana’o’i wanda zai tallafa musu wajen dogaro da kawukansu tare da bayar da na su gudummawar ga ci gaban jihar.