Hukumar gudanar da Jami’ar ‘Maryam Abacha American University (MAAUN)’ dake Maradin Jamhuriyyar Nijer, ta mika sakon ta’aziyyarta ga iyalai, ‘yan’uwa da kuma abokan arziki bisa rasuwar Malam Jamilu Sambo, wanda yake Malami ne a sashen sanin halayyar dan Adam ta Jami’ar.
Malam Jamilu ya rasu ne yana da shekara 54 a duniya a ranar Alhamis 6 ga watan Agustan 2020 a asibiti bayan gajeran rashin lafiya.
Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, shugaban Jami’ar ta MAAUN ya mika ta’aziyyar ne a cikin wata takardar sanarwa da ya rabawa ‘yan jarida a ranar Juma’a a Kano a ranar Juma’a.
Abubakar-Gwarzo ya bayyana rashin Malam Jamilu Gambo a matsayin rashi ne ga jami’ar baki daya ba kawai ga iyalansa ba. “a yau mun sake rasa wani jajirtacce, Malam Jamilu Sambo, jigo a sashen sanin halayyar dan Adam, na Jami’ar MAAUN”. Inji Farfesa Gwarzo.
Abubakar-Gwarzo, har wala yau ya bayyana Malam Jamilu Gambo a matsayin cikakken mutum, inda ya yi addu’ar Allah ya jikansa da Rahama, ya kuma bai wa iyalai da ‘yan’uwa hakurin jure rashinsa.
Marigayin ya rasu ya bar matarsa, da ‘ya’ya uku, inda tuni aka bizne shi kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a garin Kano.