By Abbas Yakubu Yaura
Shugaban babbar jam’iyyar adawa ta PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu, ya ce rashin shugabanci nagari ya gabatar da Najeriya a gida da waje a matsayin kasa mai rabe-rabe.
Ya ce shugabancin jam’iyyar APC mai mulki ta kasa yin amfani da arziƙin ’yan Najeriya iri-iri don samun ingantacciyar rayuwa wanda ya kamata ya ƙarfafa ’yan’uwantaka da inganta zaman lafiya.
Ya ci gaba da cewa kamata ya yi a sauya salon mulkin da bai dace ba a gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC wanda ya ce ya jawowa kasar nan koma baya ta fuskar tattalin arziki.
A cewar Ayu, hanya daya tilo da hakan za ta kasance ita ce a ba wa jam’iyyar PDP goyon baya wajen ganin ta samar da shugabanni na gaba a kasar nan.
Ayu ya bayyana haka ne a wajen cin abincin dare da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shirya wa gwamnonin jam’iyyar PDP a dakin taro na Banquet Hall na gidan gwamnati da ke Fatakwal, a daren Lahadi.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai taken, ‘Tabbas PDP za ta samar da shugaban Najeriya mai zuwa –Ayu,’ mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Ribas kan harkokin yada labarai, Kelvin Ebiri, a ranar Litinin.
“Dole ne mu canza wannan labari kuma hanya daya tilo da za mu canza wannan labari yin amfani da gaskiya bawai kawai al’adu ba amma muhalli da wadatar da ke cikinta shine mu marawa jam’iyyar PDP baya wacce ta kuduri aniyar samar da sabon shugabanci ga kasar nan,” in ji shi.
Ayu ya bayyana imanin cewa Najeriya za ta sake dawowa tare da PDP a kan sirdi saboda aikin ceton kasar da kuma inganta ta abu ne mai yiwuwa.
Shugaban jam’iyyar PDP na kasa ya bayyana cewa shugabancin da ake sa ran za su bayar a matakin kasa zai canza munanan halaye da ke da alaka da jam’iyyar APC da aka yi amfani da su wajen kara rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan Najeriya a kasar.
A jawabinsa na maraba, Gwamna Wike ya ce taron abin alfahari ne ga taron gwamnonin PDP da aka saba yi na karba-karba.
Ya bayyana cewa, ana amfani da irin wadannan tarurrukan ne a kodayaushe domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi yadda za a tsara al’ummar Najeriya marasa kyau.
“Ya kasance al’ada ce ga gwamnonin PDP su taru su gana su tattauna batun jin dadin jam’iyyar. Kuma wannan ya kasance yana juyawa daga wannan jiha zuwa waccan,” inji shi.
Gwamnonin da suka halarci bikin daren sun hada da, Okezie Ikpeazu (Abia), Ahmadu Umaru Fintiri (Adamawa), Udom Emmanuel (Akwa Ibom), Mohammed Bala (Bauchi), Samuel Ortom (Benue), Seyi Makinde (Oyo) da Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu) ).
Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da mataimakan gwamnonin Rivers da Zamfara, Dokta Ipalibo Harry-Banigo da Mahdi Aliyu Mohammed Gusau; Sakataren PDP na kasa, Sanata Sam Anyanwu da wasu jiga-jigai da dama.