By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Neja ta sanya dokar hana fita a wasu al’ummomi domin rage ayyukan ‘yan fashi.
Wakilinmu ya tattaro cewa gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita a wasu garuruwan kananan hukumomin Rafi da Shiroro na jihar Neja inda ake yawan kai hare-haren ‘yan bindiga.
An kafa dokar ta-bacin ne sakamakon tattara bayanan sirri da aka samu kan zirga-zirgar ‘yan fashi a kananan hukumomin da lamarin ya shafa.
An tattaro cewa dokar hana fita a al’ummar da lamarin ya shafa ta fara ne daga karfe 5 na yamma zuwa karfe 10 na safe a kullum har sai an sanar da hakan.
Da aka tuntubi Kwamishinan Kananan Hukumomi, Masarautu, da Tsaro na cikin gida, Emmanuel Umar ta wayar tarho, ya ce an dauki matakan ne domin dakile ayyukan ‘yan fashi daga al’ummomin da abin ya shafa.
“Muna da rahotannin sirri game da wani motsi da muke sa ido a kai a cikin al’ummomin da abin ya shafa,” in ji shi.
Umar ya ce an dauki matakin ne domin gudun kada maharan da ke kai hare-hare a wasu al’umma a makonnin da suka gabata.
Kwamishinan ya yi kira ga al’ummar da abin ya shafa da su ba jami’an tsaro hadin kai domin suna yin duk mai yiwuwa na dan Adam wajen dawo da zaman lafiya a yankin.
Ya kara da cewa “Wannan gwamnatin ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai duk wadanda suka rasa matsugunansu sun dawo lafiya zuwa mahaifar kakanninsu.”