A yanzu haka dai yayin da ya rage kwanaki 17 kacal a gudanar da babban zaben shekarar 2023, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya gana da mai baiwa Shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya) a ranar Talata, Punch ta rawaito.
KARANTA WANNAN LABARIN: Da Dumi-Dumi: Masu Zanga-Zangar Sun Toshe Kofar Shiga CBN
Wannan na iya zama baya rasa nasaba da karuwar kalubalen tsaro da ke addabar kasar.
A wani labarin kuma, Ten Hag Ya Bayyana Yan wasa 3 Da Ba Zasu Fafata Wasan United Da Leeds Ba
Kocin Manchester United Erik ten Hag ya yi karin haske dangane da yan wasan kungiyar dake fama da rauni gabanin wasan sh na ranar Laraba a gasar Premier League. Kamar yadda Daily Post ta ruwaito.
Antony ba zai samu fafata wasan ba bayan an cire shi a wasan da United ta sha da kyar a hannun Crystal Palace da ci 2-1 a ranar Asabar din da tagabata.
Ten Hag ya kuma bayyana cewa Martial da Scott McTominay ba su murmure daga raunin da suke fama da shi ba.
“Martial da McTominay ba za su samu damar fafata wasan yau ba.
“Kana Antony don Santos ba zai fafata wasan na yau ba, don haka ya kamata musan mafita” inji Ten Hag.