A ranar Juma’a da misalin karfe hudu na yamma rigima ta kaure tsakanin ’yan sandan garin Dandume da kungiyar ’yan sa kai na garin na Dandume da ke jihar Katsina. Wannan rigimar ta samo asali ne a lokacin da ’yan kungiyar su ka kamo wadansu Fulani guda 25, wadansu a ke zargin su da aikata ta’addanci a yankin, inda kungiyar ’yan sa kan su ka kashe mutum hudu daga cikinsu, sauran mutum 21 su na hannun ’yan sandan. Wakilinmu ya ziyarci garin Dandume domin gano abinda ya faru tsakanin kungiyar da jami’an ’yan sandan, inda ’yan kungiyar su ka nemi da hakumar ’yan sandan su ba su sauran mutanen da su ke zargi da ta’addancin, amma ba su ba su ba Wakilinmu ya zanta da wasu mutane, inda su ka bayyana mashi cewar, akwai wadansu daga cikinsu ba ’yan ta’adda ba ne, domin su na zaune da su shekara da shekaru kuma ya kamata a gabatar da bincike a kansu kafin a zartar masu da hukunci. Wannan lamari ya yi kamari sosai, domin an samu asarar rai, inda a ka kashe jami’in dan sanda guda daya. Tuni jami’an ’yan sanda su ka yi kokarin kwantar da rigima, saboda tunda misalin karfe 8:00 na dare jama’ar garin Dandume su ka shiga gidajensu, saboda ’yan sanda su na ta harbin iska, domin tsorata jama’a, don gudun tashin hankali tsakanin ’yan sanda da mutanen gari. Har zuwa jiya Lahadi lokacin hada wannan rahoto, al’ummar garin hankalinsu ba a kwance ya ke ba, saboda jin tsoron shigowar ’yan ta adda garin, domin ‘yan ta’addar sun shiga kauyakun kkaramar hukumar ta Dandume, inda a ka yi ta karon batta tsakanin ’yan sa kan da ’yan sanda da ’yan ta’adda a yankin. Wakilinmu ya sami labarin cewa a ranar Juma’a a na sallar Juma’a ’yan ta’addar sun kai farmaki a wani kauye da a ke kira Albasu da ke cikin karamar hukumar Sabuwa kusa da Dandume, inda wadannan maharan su ka kai farmaki daban-daban ya kai sau uku a wannan kauyen, inda su ka taba kashe mutum biyu kuma su ka yi garkuwa da mutane da yawa domin neman kudin fansa kuma su ka kara kai farmaki a wani kauyen a na yin sallar Juma’a a ka yi dauki ba dadi da su da ’yan sa kai. Wannan rashin tsaro ya addabi mutanen wadannan kananan hukumomi guda biyu na karamar hukumar Sabuwa da Dandume. Don haka su yi kira ga gwamnati da ta taimake su da jami’an tsaro, musammam sojoji a kai su wannan yankin su zauna, domin samo tsaro da zaman lafiya, kuma su tashi tsaye da addi’oi a kullum domin samun sauki a yankunan nasu.