A ranar Larabar da ta gabata ne Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya Usman Baba, ya mayar da kwamishinan ‘yan sandan jihar Filato, Edward Egbuka zuwa hedikwatar rundunar tare da maye gurbinsa da Bartholomew Onyeka.
An dai gano cewa sake tura Egbuka aiki bai rasa nasaba da rikicin da ya dabaibaye majalisar dokokin jihar Filato wanda aka ce an tsige kakakin Majalissar Abok Ayuba tare da maye gurbinsa da Yakubu Sanda.
Kakakin rundunar Yan sanda na Kasa Frank Mba, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce rundunar ta shirya tsaf domin samar da ingantaccen aikin ‘yan sanda a Filato da kuma fadin kasar nan.
Ya ce nadin Onyeka ya fara aiki ne nan take.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sunayen Wadanda Sukayi Nasaran Samun Aikin Hukumar Kwastom
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Shugaban rundunar ‘yan sandan, yayin da yake tabbatar wa al’ummar Jihar Filato irin jajircewar da shugabannin ‘yan sanda ke yi na dakile laifuka da suka kunno kai a jihar, ya bukaci sabon kwamishinan ‘yan sandan da ya nuna kwarewarsa wajen gina al’umman jihar, don ganin an samu ci gaba. Ta hanyar tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa a jihar.
“Ya kuma umarci al’ummar Jihar Filato da su ci gaba da yin aiki tare da ‘yan sanda domin gudanar da aikin ‘yan sanda a yankunansu.”
Sabon Kwamishinan ya fito ne daga Nkume, a karamar hukumar Njaba ta jihar Imo, kuma ya yi digirin B.A (Hons) a fannin harkokin gwamnati da kuma digiri na biyu a fannin tsaro daga jami’ar Punjab ta kasar Indiya.
Comments 1