Daga: Abbas Yakubu Yaura
A kokarin sulhunta dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike kwamitin amintattu (BoT) ya kafa kwamitin kowa da kowa.
Ku tuna cewa sansanin Atiku da Wike na cikin yakin basasa tun bayan zaben fidda gwani na jam’iyyar da kuma kaddamar da gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Neja: Gwamna Sani Bello Ya Koka Da Karancin Tallafi Na Tsarin Bayar Da Gudummawar Kiwon Lafiya A Jihar
Da yake zantawa da manema labarai a karshen taron BoT da ya kwashe kusan sa’o’i 4 ana yi a Abuja, tsohon dan majalisa, Sanata Abdul Ningi ya ce ana sa ran kwamitin zai yi musabaha tsakanin sansanonin da ke fada da juna.
Ya ce, “mun kafa a wannan kwamitin taron na BoT don samun damar yin mu’amala tsakanin bangarorin da ke gaba da juna.”
“Musamman rikicin da ke faruwa tsakanin dan takarar shugaban kasa da Gwamna Wike.”
Ningi ya ce ana kuma sa ran kwamitin zai sasanta wasu rigingimun da ke faruwa a jam’iyyar a fadin kasar nan.
“Kwamitin shine kwamitin gaba daya, ma’ana kowanne memba na BoT mamba ne na kwamitin.”
“Ba zan iya gaya muku korafe-korafe da kuma lokacin da aka yi ba,” inji Ningi.
Dangane da ko an tattauna batun yin murabus na shugaban PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu a taron BoT, Ningi ya ce: “Ba mu ma tattauna wani batu na wani ya sauka ba. Abin da muka tattauna shi ne abin da na gaya muku”.