Rundunar ‘yan sandan ƙasa, a yau Asabar, ta ce harabar majalisar dokokin jihar Filato za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai an warware dukkan matsalolin da suka dabaibaye ta.
Mataimakin Sufeto-Janar na ‘yan sanda mai kula da shiyya ta 4, Moustapha Dandaura, ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron sulhu da ‘yan majalisar dokokin jihar, wanda aka gudanar a rikicin ‘yan sanda a Jos.
DUBA WANNAN LABARIN: 2023: Yan Katsina da Daura Sun Bukaci Gwamna Yahaya Bello ya Fito Takara
Jaridar Dimokuraɗiyya ta rawaito cewa cewa dukkan ‘yan majalisar 24 ne suka halarci taron.
Suma shugabannin majalisar, tsohon da kuma sabon Hon Sanda Yakubu da wanda aka tsige, Abok Ayuba Nuhu, a yayin taron, sun yi ikirarin cewa kowannen su ne shugaba, kuma anan ne tsohon kakakin majalisar ya ce an janye duk wasu jami’an tsaron da aka bashi.
Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, AIG Dandaura ya ce, Sufeto Janar na ‘yan sandan ya damu da abubuwan da ke faruwa a majalisar, inda ya bayyana cewa taron an yi shi ne domin samar da zaman lafiya a tsakanin bangarorin domin ganin an dawo da harkokin ‘yan majalisa domin maslahar jihar.
AIG ya umurci ’yan majalisar da su koma su sake gudanar da wani taro a cikin su sannan su kai rahoto ga ‘yan sanda kudurinsu domin jihar ta ci gaba.
Idan dai ba a manta ba a makonni biyu da suka gabata ne wasu ‘yan majalisar da ke zaman majalisar suka sanar da tsige Abok, inda suka zabi Sanda a matsayin sabon shugaban majalisar, lamarin da ke janyo cece-kuce a cikin ‘yan siyasar jihar.
Comments 1