Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Liberpool, Muhammad Salah, ya bayyana cewa yana girmama dan wasa Ronaldo saboda irin tarihin daya kafa a duniya kuma bai kamata mutane su dinga tunanin hada shi da dan wasan ba saboda kowanne acikinsu salon buga wasansa daban ya ke. Salah, mai kwallaye 3 a gasar zakarun turai ya bayyana cewa wasa na biyu da zasu fafata a tsakanin FC Porto da Liberpool ba karamin wasa bane kuma zasuyi iya kokarinsu wajen ganin sun samu nasara idan sunje Portugal. Ya cigaba da cewa da shi da ‘yan wasan kungiyar ta Liberpool ne sukayi aiki tukuru sukaga sunzo wannan mataki kamar yadda kowacce kungiya tazo kuma bazasu bawa magoya baya kunya ba. Ya ce yana buga wasa a babbar kungiya a duniya mai cike da tarihi da nasarori kamar yadda shima Ronaldo yake bugawa babbar kungiya a duniya mai cike da tarihi da burin lashe manyan kofuna sai dai ronaldo din ya lashe kofunan da bai taba lashewa ba. Ya ci gaba da cewa babu dan wasan da zai iya kai wata kungiya wasan karshe shi kadai dole sai da hadin kan ragowar yan wasa da magoya baya da kuma mai koyarwa da shugabanni da kuma likitoci amma Ronaldo yana iya yin wannan bajinta saboda haka dan wasane ba kamar kowa ba. Salah ya ce, ya na fatan lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallo na duniya na shekara mai zuwa inda yace yasan duka larabawan da suke duniya suna goyon bayansa domin ganin ya zama babban dan wasa kuma yana alfahari da yadda yake samun goyon baya. A karshe kuma yace yana fatan ‘yan wasan kungiyarsa zasu cigaba da dagewa domin ganin sun kafa tarihin lashe gasar firimiyar Ingila bayan da kawo yanzu sune a mataki na farko akan teburin gasar da tazarar maki daya a tsakaninsu da Manchester City sai dai City din tanada kwantan wasa daya bayan kowa ya buga wasa na 33.