Ministan Sufurin Tarayya Rotimi Amaechi ya ce babu abinda raba kasar nan ko sake mata tsari zai haifar idan ba koma baya ba.
Amaechi ya kara da cewa rashin adalci ne a dora alhakin tabarbarewar al’amuran kasar nan kan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.
Har ila yau ya ce babu yadda za a yi kasar nan ta ci gaba muddin yan kasa ba su nuna kishi da son juna ba.
Amaechi yana wadannan kalamai ne a yayin gabatar da wata Lakcha a gurin taron fadakarwa na Jami’ar Kalaba mai taken “Abinda Ya fi KArfin mu: Ayoyin tambaya kan kasar nan da Kuma alkiblar Kasar.
Ministan ya ce matsalar fatara a kasar ba za ta kau muddin ba a magance matslar talauci da sauran rashin kshin kasa ba.
Da yake tsokaci Shugaban Jami’ar Kalaba Farfesa Florence Obi ya jinjina wa Ministan bisa samun halartar taron inda ya alkwarta cewa jami’ar za ta ci gaba bunkasa harkar ilmin jami’o’i a bangaren ta.