Babban Kwamandan runduna ta daya dake Kaduna, Birgediya Janar Jimmy Akpor, a ranar Alhamis sun mika wa gwamnatin Kaduna shanu 134 wanda ake zargin ‘yan bindiga ne suka sace su.
Su dai wadannan dabbobin da adadinsu ya kai 134 an mika su ne ga jagoran ‘Operations Yaki,’ Mai ritaya AIG Murtala Abbas a kauyen Kakau dake karamar hukumar Chikun. Akpor ya ce; suna mika wadannan dabbobin ne da suke zargin sato aka yi wanda kuma suka kwato su a karkashin atisayen ‘Thunder Strike’ ga wakilan gwamnatin jihar Kaduna.
Rahotanni sun bayyana cewa; dabbobin sun hada da shanu 120, da tumakai 14 wadanda aka kwato su daga hannun masu garkuwa da mutane da suka addabi titin Kaduna zuwa Abuja.
Wanda ake zargin da harkar garkuwa da mutane, Aminu Mallam wanda aka fi sani da Baderi, an kama shi ne a kauyen Sabon Gayan a karamar hukumar. A ranar 2 ga watan Satumba ne, atisayen ‘Thunder Strike,’ daga sojin runduna ta 1 suka kai hari a sansanin masu garkuwa da mutanen a kauyukan Ligari da Sabon Gayan. Sannan kwanaki kadan da kai wannan hari, aka gano shanun a yankin Ligari din.
Rundunar sun ce sun samu bayanai daban-daban na sirri ne kafin su kai wannan samamen. Sojin sun ce abin takaicin da suka gano shi ne, wadannan barayin suna hayar matasan da ba su ji ba su gani ba wajen kiwon wadannan dabbobin da suka sato.