Rundunar Sojin Ƙasa ta ƙaryata Sunayen dake yawo cewa ta Ɗauki Soji Kashi na 83
Rundunar Sojin Ƙasa ta ƙaryata wani adireshin daya sanar daya fito da Sunayen Mutanen da suka samu nasarar samun aikin Soji kashi na 83, inda ta bayyana shi a matsayin Ƙarya ne.
Daraktan Jami’in Hulɗa da Jama’a na Sojin Birgediya-Janar Onyeama Nwachukwu a cikin wata sanarwa daya fitar a Abuja a ranar Alhamis, yayi gargaɗi ga Al’umma dasu zama masu kula da ƴan Damfara.
KARANTA WANNAN LABARIN: An cafke Kansila da AK-47 kusa da Maɓoyar Ƴan bindiga a Kaduna
Nwachukwu ga bayyana cewar wannan sunayen da aka fitar ba komai bane illa Damfara da aiki masu Damfara, wanda suka ƙware wajen cutar Al’umma.
“Ana sanar da Al’umma cewa Adireshin da za’a ɗauki Jami’an Soji kashi na 83 an buɗe shi ne a ranar 7 ga watan Maris kuma har yanzu yana nan buɗe.
“Za’a kuma a kulle a ranar Juma’a 13 ga watan Maris.
“A saboda haka wannan wallafaffen sunaye dake yawo a Kafafen Sada Zumunta a jefar dashi”, Inji shi
Comments 1