Rundunar sojin kasar Mali ta ce wasu ‘yan kasar China uku da aka yi garkuwa da su a watan Yuli ‘sun kubuta daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su. A wani yunkurin sojin Kasar.
Rundunar sojin ta kubutar da mutane ukunne daga hannun Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai a wani gini dake kudancin kasar.
Kazalika rundunar sojin ta ce, ta Kuma kubutar wasu ‘yan kasar Mauritaniya biyu da aka sace a lokaci guda bayan kwanaki 10.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ‘yan bindigar sun yi nasarar kubutar da su a ranar Lahadin da ta gabata, kuma an gano su ne a washegari a wani farmakin hadin gwiwa da ya hada da sojojin kasa da na sama.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ma’aikata 6 Akayi Garkuwa da su a Jami’ar Abuja~ Rundunar Yan sanda
Rahotanni sun Kuma bayyyana cewa, mutanen suna cikin koshin lafiya.
A wani Labarin Kuma na daban.
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa rikicin sauyin yanayi yana zama barazana ga yara biliyan daya, lamarin dake jefa su cikin hadari.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Litinin, inda ta bayyana cewa UNICEF zata halarci taron na COP26 domin tabbatar da cewa an amince da hakkin Kananan yara a matsayin wani bangare na rikicin sauyin yanayi.
Babban Daraktar na UNICEF, Henrietta Fore, tace, “Dole ne COP26 ya zama COP na yara. Sauyin yanayi na daya daga cikin manyan barazanar da wannan tsara ke fuskanta, inda yara biliyan 1 ke cikin hadarin gaske.Duk da haka, yayin da ra’ayin ya kasance mai tsanani, shugabannin duniya a COP26 suna da muhimmiyar dama mai mahimmanci na lokaci don karkatar da mummunar hanyar da muke tafiya akai.
“Za su iya yin hakan ta hanyar yin alkawarin ƙarfafa juriyar ayyukan da yara suka dogara da su, da kuma rage fitar da hayaki cikin sauri Makomar biliyoyin yara ya dogara da shi.”
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa kimanin yara biliyan daya, wadanda ke wakiltar kusan rabin yaran duniya suna rayuwa a kasashe 33 da aka ware a cikin Index a matsayin “masu hadarin gaske”.
A cewar UNICEF, irin waɗannan yara suna fuskantar bala’in sauyin yanayi da muhalli tare da babban lahani ga rayuwar su saboda rashin isassun ayyuka masu mahimmanci, kamar ruwan sha da tsaftar muhalli, kiwon lafiya da ilimi.UNICEF ta lura cewa kasancewarta a taron COP26 an tsara shi ne don inganta hanyoyin da za a rage haɗarin yanayi ga waɗanda suka fi rauni.