Rundunar sojin Najeriya ta ce babu bukatar a firgita bayan faruwar wasu fashe-fashe da suka afkawa a cikin wasu al’ummomi da ke Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya sanyawa hannu, rundunar ta bayyana harin a matsayin “shirin tsaron da ake zargin ‘yan ta’addan Boko Haram ne (BH) da kuma ‘yan ta’addan (ISWAP) da suka yi yunkurin aiwatarwa da karfin tuwo a safiyar ranar Lahadi, 4 ga watan Disambar 2021, tare da fashe-fashe a wajen birnin Maiduguri.”
Rahotanni sun bayyana cewa fashe-fashen sun faru ne a cikin al’ummar Gomari da kuma Gidaje 1,000 Estate, a Maiduguri amma ba a sami asarar rai ba.
“Wannan mummunan lamari ya haifar da barna da fargaba a wuraren zama. Ko da yake, ba a rasa rai ba, abun bakin ciki ne wani dan karamin rauni ya samu,” in ji rundunar.
“Dakarun kasa tare da hadin gwiwar AC na OPHK sun mayar da martani cikin gaggawa tare da mamaye yankin tare da yin katsalandan na kasa da na sama wanda ya yi nasarar kawar da barazana da yunkurin kutsawa daga ‘yan ta’addan.
“An yi kira ga jama’a da kada su firgita saboda sojoji suna nan kuma sun mamaye birnin don kawar da duk wata barazana da ake ganin zata iya faruwa.
“An kuma umarci mutanen Maiduguri nagari da su cigaba da gudanar da harkokinsu na tattalin arziki da kuma samar da bayanan da suka dace game da motsin wadannan miyagu.”