Rundunar sojin ta kasa ta ce, ta yi nasaran kashe sama da yan bindiga 20 a wani hari da ta kai mafakan su a jiya lahadi, da ke dajin Lambua na jihar Borno.
Wannan na zuwa ne kwanaki uku bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ziyarci jihar, inda ya umarci rundunar data kara tura jami’an ta, zuwa wurare daban da daban, domin kare wuraren noma.
A cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun rundunar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce rundunar ta sami nasarar kwace makamai a hannun yan bindigan.
Sanarwar ta ce, an kai wa yan ta addan harin ne ta sama da kasa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kutu ta tura da mutun uku gidan gyaran hali
Rundunar ta kuma kwace mungwan makamai, wanda suka hadar da: Bindigan harbo jirgin sama guda uku, kunshin harsashin AK-47 guda uku, da kuma tankar yaki guda biyu, bayan wasu mungwan makaman da rundunar ta lalata a maboyar yan ta’addan
A karshe shugaban rundunar sojin Faruk Yahaya, ya yaba da nasaran da rundunar ta yi. Inda kuma ya umarci su, da su cigaba da kai farmaki ka yan bindigan.
Comments 1