Rundunar yan sandan Nigeria za ta dauki Sabin jami’ai guda 60,000, a cikin shekaru shida masu zuwa.
Babban sufeton yan sandan Nigeria IGP Usman Baba ne ya bayyana hakan, a yau Laraba yayin ziyarar aiki da ya kai ga rundunar yan sandan jihar Kwara a Ilorin, babban birnin jihar.
Wannan shi ne daidai lokacin da shugaban yan sandan ya bayyana Kwara a matsayin jiha mafi zaman lafiya a fadin kasar nan, idan aka kwatanta da sauran jihoh dake Nigeria.
Kazalika sifecton ya ce, rundunar yan sandan za ta dauki sabbin jami’ai akalla 10,000 a kowace shekara, har na tsawon shekaru shida.
KARANTA WANNAN LABARIN: Majalissar Dokokin Kaduna ta tsige Shugaban Masu rinjaye
“Shugaba Muhammadu Buhari ya ba mu izini mu dauki jami’an‘ yan sanda 10,000 a kowace shekara, har na tsawon shekaru shida masu zuwa nan gaba. Kuma Mun fara amma ba mu yi ba a shekarar 2020. Don haka, za mu dauki na shekarar 2020 da 2021 tsakanin yanzu zuwa nan dan karshen shekara nan. Inda za su sami horo na tsawan watanni shida. Don haka Muna saran nan da zuwa karshen shekarar 2021, za mu Sami Karin jami’ai 20,000 a cikin rundunar Yan sanda ”inji Baba.
Ya kara da cewa za a dauki sabbin jami’an ne daga kananan hukumomi 774 dake fadin kasar nan, inda ya kara da cewa, bayan kammala horas da su, a na duba yuwuwar tura jami’an zuwa jihohin su na asali domin bada gudun mawa wajan wanzar da zaman lafiya a Nigeria.
Tun da farko, a nasa jawabin, Kwamishinan yan sandan jihar Kwara, Mr Tuesday Assayomo ya ce, rundunar yan sandan jihar, ta na fama da karancin jami’ai, inda take da jami’an yan sanda Maza guda 3,500 kacal.
A wani labarin Kuma na daban
Kungiyar Taliban ta mayar da martani kan ikirarin mayakan da ke da alaka da kungiyar IS, kan zargin da ake cewa, IS ta mamaye lardin Kunduz na kasar Afghanistan.
Hajji Najibullah Haron, babban jami’in leken asirin kungiyar Taliban ya ce, IS ba ta mamaye lardin Kunduz na arewacin Afghanistan ba.
Kamfanin Dillancin Labaran Nigeria NAN, ya ruwaito cewa,Haron ya bayyana rahotannin a matsayin marasa tushe da balantana makama.
Da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar yau Laraba, ya ce: “Zaman lafiya na din-din-din ya dawo lardin Kunduz kuma mutane na zaune cikin kwanciyar hankali a can, kanazalika duk wani rahoto game da kasancewar yan ta’addar IS a Kunduz ba gaskiya bane.” a cewar shi.
Ya jaddada cewa sabuwar gwamnatin Afganistan, ba za ta bari kowa ya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaro a Kunduz, ko wani yanki na kasar ba.
Kwanan nan kungiyar Taliban ta karbe ikon gwamnatin Afghanistan bayan ta karbe ikon Kabul Babban birnin kasar.