‘Yan kasuwa a jihar Kaduna sun fara gudanar da addu’o’i na musamman a kan gwamnatin jihar Kaduna sakamakon manufar gwamnan jihar na rusa wasu manyan kasuwannin jihar tare da sake gina su a tsarin ginin zamani.
Rahoton jaridar Daily Trust ta labarto ‘yan kasuwan na bayyana rashin gamsuwarsu da manufar gwamnatin na zamanantar da kasuwanni, musamman duba da cewa ba ta ba su wani wurin da za su ci gaba da gudanar da kasuwancinsu ba.
A cikin wata hira da aka yi da gwamnan jihar Kaduna, ya tabbatar da burinsa na fadada wasu kasuwannin jihar tare da zamanantar da su, da suka hada da Kasuwar barci, kasuwar Sabon gari da kuma babbar kasuwar Kaduna na Sheikh Gumi.
Gwamnan ya ce; “Kasuwannin nan suna bukatar a fadada su, kuma zamu fadada su, kuma zamu gina sabbin kasuwanni na zamani a unguwanni inda mutane za su iya kama hayan shaguna, daga nan zamu wuce Zariya da Kafanchan don gina sabbin kasuwanni, dole ne kawai mu gyara Kaduna.” Inji shi. Haka zalika Gwamnan ya kara da cewa za su gina sabbin kasuwanni a garin Rigasa na karamar hukumar Igabi, da kuma garin Zonkwa.
Sai dai wasu daga cikin ‘yan kasuwan sun bayyana damuwarsu game da wannan aiki, musamman ‘yan kasuwan barci, wanda suka ce sun fara addu’ar ka da Allah ya bai wa gwamnan ikon aiwatar da wannan manufa.
Wani Tela dake kasuwar barci, Sani Muhammad ya bayyana cewa: “Mun fara addu’o’i na musamman a kan wannan manufa, saboda yawancinmu muna cikin damuwa game da aikin, saboda zamu rasa abin yi idan aka fara aikin.”
Shi ma wani mai suna Jafaru Madobi ya ce: “Wannan zalunci ne, saboda a yanzu haka duk mun dimauce, mun sani idan aka rusa kasuwan ba zamu sake samun shago ba, mu jari muke so daga wajen Gwamnan ba aikin fadada kasuwa ba.”
Haka zalika wani dan gwanjo mai suna Usman Mani ya ce: “Mun shiga damuwa tun bayan maganar da gwamnan ya yi saboda bamu da na yi, me yake su mu yi, tun da yawancin bamu da kudin da zamu iya kama shago? Kuma bamu ji ya yi maganan biyan kudin fansan shagunan da zai rusa ba.”