Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu a wani bene mai hawa 22 da ya ruguje a Legas, yayin da wasu ke makale.
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Mista Femi Adesina, ya fitar a ranar Litinin a Abuja, ta ce shugaba Buhari ya taya al’umma bakin ciki da kuma gwamnatin jihar Legas, inda ya bukaci hukumomi su kara kaimi wajen ayyukan ceto.
Ya yi kira ga cibiyoyin bada agajin gaggawa da suka hada da asibitoci da su ba da duk wani tallafi da ya dace domin kare rayukan wadanda aka ceto.
Shugaban ya yi addu’ar Allah ya kawo dauki cikin ayyukan ceto da ake ci gaba da yi.