Gwamna jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ya ayyana kwanaki uku na zaman makokinba jihar, domin nuna alhini kan wadanda suka rasa rayukan su sakamakon rugujewar ginin Ikoyi, wanda ya afku a ranar Litinin.
Gwamnatin jihar ta yi ikirarin cewa a kalla mutane 32 ne ake kyautata zaton sun mutu a lamarin, yayin da jami’an ceto ke cigaba da aikin laluben wajen da ginin ya rufta.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai Gbenga Omotoso ya rabawa manema labarai a ranar Alhamis.
“Gwamna Sanwo-Olu ya ziyarci wurin har sau uku domin karfafa gwiwar masu aikin ceto tare da jajanta wa wadanda ake kyautata zaton sun makale a ginin mai hawa 21.”
DUBA WANNAN LABARIN: Zamfara: Ƴan sanda sun Kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su
“Yau ya je asibitin ne domin taya wadanda suka jikkata jimami bisa wannan abun alhini da ya faru ga yan’uwansu, kafin ya rantsar da kwamitin bincike na mutum shida domin gano dalilin da ya sa ginin ya ruguje tare da ba da shawarar daukar matakan hana faruwar hakan.” A cewar sanarwar.
A ranar Alhamis ne Sanwo-Olu ya kaddamar da mambobin kotun binciken da za ta gudanar da bincike kan dalilin da ya haddasa rugujewar benen mai hawa 21 a kan titin Gerrard a Ikoyi ranar Litinin.
Comments 1