By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar jin kai da kula da bala’o’i da ci gaban al’umma ta bayar da umarnin kai daukin gaggawa domin gudanar da ayyukan ceto a wurin ginin bene mai hawa 21 da ya ruguje a ranar Litinin a Unguwar Ikoyi dake Legas.
Ma’aikatar Agaji da kula da Bala’oi da Cigaban Jama’a,karkashin jagorancin Sadiya Umar Farouq, ta bayyana kaduwarta kan lamarin a daidai lokacin da ta jajanta wa jama’a da gwamnatin jihar Legas.
Ta umurci tawagar Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa daga ofishin jihar Legas dasu taimaka da ayyukan ceto a wurin.
Mai baiwa Ministan shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Nneka Ikem Anibeze shine wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar ranar Litinin.
An ambato Ministan tana cewa, “Wannan abin takaici ne. Ina jajantawa gwamnatin jihar Legas da iyalan mutanen da har yanzu ke makale a cikin baraguzan ginin.
“Mun tattara ayyukan ceto cikin gaggawa ta hannun Hukumar NEMA daga ofishin mu na jihar Legas domin hada kai da hukumar SEMA ta jihar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “NEMA ta kuma taimaka wajen tattara kayan aiki daya hada da na’urori masu nauyi don ayyukan ceto da kuma tsaro don shawo kan jama’a.