Yanzu masu garkuwa da mutane a Kano sun canza taku. Abin da ya faru ga ‘yar uwata yayin da za ta dawo daga asibitin International Clinics da ke Sabon Gari, misali ne.
Ranar nan mijinta ya kai ta asibiti don ta yi awo da nufin bayan ta gama za ta wuce gidan mahaifiyarta don haka sai ya ce mata ta dauki A daidaita sahu (Keke Napep) saboda ba zai samu damar dawo da ita gida ba.
Tun kafin ta fita daga motar, mijin nata ya umurce ta da ta kashe wayarta saboda kar ta je wajen likita ana kiranta. Ai kuwa ta kashe wayar, maimakon ta sa a jaka, sai ta daure a karshen zaninta.
Bayan ta kammala da asibiti sai ta fito ta tari mai A daidaita a kan ya kai ta Goron Dutse. Suna cikin tafiya, sai mai A daidaitan ya roke ta, don Allah bari ya kai sako a kan hanyarsu. Ai kuwa sai ga su a wani katon gida. Suna zuwa ya yi waya, wai ga sakon ya kawo. Aka bude gida, ya shiga da ita.
Nan da nan ta budi baki ta ce: me za mu yi kuma a nan? Ai kuwa a nan take sai ta ji duka ta ko’ina. Suka fito da ita daga A daidaitan suka dinga dukanta sai da ta wahala sannan suka tambayi wayarta.
Ta ce ba ta da waya cikin kuka. Suka duba jakarta babu waya. Suka ce, waye mijinta? Ta ce, mai shara ne a asibitin da ta fito, wajensa ta je. Suka ce, waye ubanta? Ta ce, maigadi ne. Sai suka ci gaba da dukanta, duk da haka ta ki gaya mu su gaskiya, ta yi ta kwarma ihu tana kuka.
Duk abin nan da ke faruwa ashe ogansu yana sama yana kallo. Sai gashi ya sauko ya zo ya dinga yi mu su fada, wai don me za su kawo masa irin wannan mata ko waya ba ta da shi saboda tsiya? Yaya za a samu wani abu wajen iyayenta ko mijinta? Ya ce su mai da ita saboda wannan kaya za ta zame mu su. Aka ce a samo wasu su zo su maida ita.
Ta ce, a wurin akwai mata birjik, kafin a zo maida ita wasu daga cikinsu suke ce mata, kin yi sa’a, an kawo ki da La’asar za ki tafi da Isha. Wasunsu suka ce sun jima a wannan wuri, ba a zo an kawo kudin karbarsu ba.
‘Yar uwar tawa ta ce, ta ga A daidaita sun fi 100 a wajen. Kuma duk aikinsu ke nan. A haka dai aka hadata da mutane biyu, daya na tukawa daya yana rufe da bakinta, sai da suka yi nisa suka ingizo ta kasa, suka gudu.
Ta tashi tana ta ihu, jama’a suka taru. Ta fito da wayarta, mutanen wajen suka kira mijinta saboda ta rude. Ashe a Rijiyar Zaki suka ajiye ta. Mijinta ya je ya dauke ta.
Na yi wannan rubutu ne don jan kunnen ‘yan uwana mata, kada ki yarda idan aka dauke ki, a ce za a ajiye sako a wani wuri.