Rahotannin da suke fitowa na nuni da cewa; dan wasan Liverpool Sadio Mane zai iya komawa Real Madrid, kamar yadda dan wasan Senegal wato Keita Balde ya tabbatar, inda ya kara da cewa zai yi wahala Sadio Mane, mai shekara 28, ya ci gaba da zama a Anfield “har abada”.
Haka zalika a wani rahoton kuma, kungiyar Barcelona za ta sake taya dan wasan Brazil Neymar, mai shekara 28, domin ta dawo da shi daga PSG.
Kungiyar ta ce a shirye take ta bayar da ‘yan wasan Faransa uku Samuel Umtiti, Ousmane Dembele da kuma Jean-Clair Todibo a matsayin yarjejeniya don karbo shi a daidai lokacin da suke fama da karancin kudi saboda annobar coronavirus kamar yadda rahoton Bbc Hausa ya tabbatar.