Sahun farko dauke da ‘yan Nijeriya 84 sun dawo gida daga kasar Afrika ta Kudu a wani mataki da gwamnatin tarayya ta dauka na kwashe ‘yan kasarta a kasar Afrika ta Kudun sakamakon rikicin kyamar baki d ya ki ya ki cinyewa.
Ana sa ran jirgin zai sauka Nijeriya da misalin karfe 2 na ranar yau Laraba a filin jirgin sama a Murtala uhammad dake Legas tare da rakiyar jami’an ma’aikatar lura da kasashen waje. Ma’aikatar ce ta bayyanawa manema labarai hakan a Abuja.
Ma’aikatar ta tbbatar da cewa mutum 313 suka nemi dawowa, amma zuwa yanzu 84 aka kammala tantancewa.