Sako zuwa ga Datti Assalafy.
Duk Addini ko Akidar da Dan Adam yake so yabi, ko yake bi, to fa lallai yana bukatar rayuwa kafin ya iya bin wannan addinin ko akidar.
Dama dai nasan cikakken sunanka ne dana maka martanin daya dace dakai, toh amma baka da sunan yanka bare na uba da zan yi amfani da shi wajen kiranka da sunan.
Toh amma tunda ka sauya wanda kake ganin kafi aminta dashi toh sai muce Allah raka daki gona.
In kana da karfin hali da har zaka yiwa Malami irin Sheikh Nuru Muhammad Khalid rashin kunya, toh kana bukatar zarra da zaka iya bayyana kanka da cikakken suna da adireshinka.
Sheikh Muhammad Nuru Khalid cikakken malamin Ahlus Sunnah ne, wanda baya bukatar amincewarka ko iyayen gidanka.
Duk kashe – kashen da ake yi a kasarnan musamman a arewacin Najeriya Malamanmu sunyi shiru wadanda kai da ire irenka da kuke da awar sune ahlus Sunnah na gaskiya.
Sheikh Albanin Gombe an dakatar dashi dan ya fadi gaskiya, Abu Ammar a katsina an kama shi sau da yawa saboda ya fitar da gaskiyar, ga misalai irin su Malam Bala Lau Malam Kabir Gombe duk basu fada ba. An kamo Sheikh Bello Yabo tun daga Sokoto har kaduna dan ya fadi gaskiya.
Inda kawai kuka fi auki shi ne inda za adora gwamna kan mumbari a yaudareshi yayi wa’azi ya bada kudi, tunda ku dai in zaku samu kudi toh rayuwar bayin Allah ba a bakin komi take ba, a wajen ku.
DUBA WANNAN LABARIN: Gwamnan Neja ya gaza bayyana gaban majalisa akan lokaci domin gabatar da kasafin 2022
Abinda kuka fi aminta dashi shi ne me yasa ake maulidi, kuma me yasa baza abari ba? Ko kai aka tambaya cewa yaushe za abar maulidi bana tunanin zaka iya bayar da amsa dai dai da tambayar da aka yi maka.
Sheikh Muhammad Nuru Khalid cewa yayi abar zagin mai maulidi ko sukar shi, domin shima mai maulidi ya daina aibata wanda baya maulidi tare da jira har muje gaban mai abun ya yiwa kowa hisabi.
Saboda haka ina mai jamaka kunne da lallai ka kula da harshenka kan wadannan kalaman da kake sukar Malaminmu dasu.