Gwamnatin tarayya ta shelanta ranakun Litini 12 ga watan Agusta da Talata 13 ga watan Agusta a matsayin ranakun hutu domin shagulgulan Sallar, Eid-Al-Kabir, 2019. Babban sakatare a ma’aikatar harkokin cikin gida, Lauya Georgina Ehuriah, wacce ta shelanta hakan a madadin gwamnatin tarayya, ta taya al’ummar Musulmi murna da wannan lokacin. Ta yi kira ga daukacin ‘yan Nijeriya da ke nan cikin gida da waje, da su yi amfani da wannan lokacin na bukukuwan Eid-Al-Kabir, wajen nuna soyayya da jin kai, zaman lafiya da sadaukarwa kamar yanda Manzon tsira Annabi Muhammadu (SWA), ya koyar da mu. Ta kuma umurci ‘yan Nijeriya da su guji duk wani nau’I na tashin hankali su hada hannu da gwamnatin tarayya wajen gina kasa wacce ke dawwame a bisa tafarkin zaman lafiya, da gina kakkarfan kasa Nijeriya, domin cimma manufofin mataki na gaba. A cewar sanarwar, wacce daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar, Mohammed Manga, ya fitar, babbar sakatariyar ta tabbatar da aniyar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya, ta kara da cewa, an umurci dukkanin hukumomin tsaro da ke karkashin ma’aikatar da su tabbatar da sun samar da cikakken tsaro, kafin, a lokacin da kuma bayan bukukuwan na Sallar ta, Eid-Al-Kabir. Lauya Ehuriah, ta taya ‘yan Nijeriya murnar da fatan gudanar da shagulgulan na Sallar Eid-Al-Kabir, lami lafiya.