Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas a ranar Asabar ya ce ko bayan shekaru 62 da samun ‘yancin kai, Najeriya na ci gaba da kokarin samun ‘yanci daga ayyukan ta’addanci da talauci.
Sanwo-Olu ya bayyana haka ne a yayin faretin zagayowar ranar samun ‘yancin kai, domin tunawa da ranar samun ‘yancin kai na tarayyar Najeriya karo na 62.
KARANTA WANNAN LABARIN: Najeriya @62: Buhari Bai Barwa ‘Yan Najeriya Abin Da Zasu Yi Murna Dashi Ba – LP
Ma’aikatar harkokin cikin gida ta jihar Legas ce ta shirya faretin da aka gudanar a filin wasa na Mobolaji Johnson Arena dake Onikan.
Ya ce har yanzu kasar na neman ‘yanci daga mummunan tasirin sauyin yanayi da kuma tabarbarewar tarbiyya.
“Shekaru sittin da biyu da suka wuce, da samun ‘yanci daga turawan mulkin mallaka, wanda muke bikin; a yau yunkurin mu shine samun ‘yanci daga ta’addanci, talauci, mummunan tasirin sauyin yanayi, da kuma tabarbarewar tarbiyya.”
“Fiye da kowane lokaci, ya zama wajibi ga matasa masu tasowa su samar da mafita mai ɗorewa ga kalubalenmu,” in ji gwamnan.
Ya ce a Legas ne labarin ’yancin kai ya bayyana a Najeriya, inda Union Jack ta sauka da Green-White-Green, wanda ke dauke da fata da mafarkin miliyoyin bakaken fata a Najeriya da sauran kasashen waje.
Sanwo-Olu ya amince da matsayin jihar Legas a cikin daukakar Najeriya, domin a ko da yaushe jihar ta kasance mai saurin tafiya.
Ya ce, da dama daga cikin ayyukan kirkire-kirkire da suka samo asali daga Legas sun zama abin koyi ga sauran jihohi da ma gwamnatin tarayya, a yunkurin hadin gwiwa na kara habaka ci gaba da samar da ci gaba a dukkan sassan kasar nan.
A cewarsa, a Legas ne sabuwar gwamnati, bayan samun ‘yancin kai, ta fara aiki mai cike da tarihi na cikakken mulkin kai.
“Tun daga wannan lokacin, Legas ta ci gaba da girma, ta kowane fanni.”
“Amma duk cikin manyan sauye-sauyen da aka samu, tun kafin samun ‘yancin kai, har zuwa wannan lokaci, abu daya bai canza ba, har yanzu mu ne tukunyar narkewar da muka kasance a kodayaushe, ga jama’a na kowane bangare na addinai, harsuna, da zamantakewa da tattalin arziki.”
“Muna maraba da kowa da kowa tare da ba su damar gina arziki da makoma ta hanyar aiki tukuru da jajircewa, samar da kananan Najeriya daga bambance-bambancen da ake nuna mana akai-akai.”
“Yau, 1 ga watan Oktoba, ta sake ba da damar sake sadaukar da kanmu don tafiya zuwa “Babbar Legas” na burinmu na gamayya.
“Muna ci gaba da jajircewa wajen mayar da jihar Legas tattalin arzikin karni na 21, jihar Smart City mai wadata da kuma yin takara a duniya. Muna da abin da ake bukata don fitar da wannan umarni,” inji shi.
Gwamnan ya ce jihar za ta ci gaba da zama matattarar ci gaban kasa a Najeriya wajen bunkasa ababen more rayuwa, masana’antu, al’adu da karbar baki, fasaha da kirkire-kirkire.
Ya ce gwamnati za ta gina jihar da za ta yi aiki ga kowa da kowa, wanda a cikinta za a samu dama daidai wa daida ga kowa da kowa don cimma burinsa na halal.
“A matsayinmu na wakilanku da masu kula da ku, za mu ci gaba da rike hannunmu a kan garma kuma mu mai da hankali kan burinmu na samar da rayuwa mai dadi, lafiya da wadata ga jama’armu.”
“A karshe, ina so in yaba wa dukkan jaruman mu na baya da na yanzu, wadanda suka yi kokari da sadaukarwa, a cikin shekaru da dama da suka gabata, da duk wadanda suka ci gaba da yin aiki da sadaukarwa a yau, don tabbatar da ‘yanci ga dukkanmu.”
“Ina yiwa daukacin mutanen Legas murnar cikar Najeriya shekaru 62 da samun ‘yancin kai. Kada aikin jarumtar mu na da da na yanzu ya kasance a banza. Allah ya taimaki jihar Legas, Allah ya taimaki tarayyar Najeriya,” inji Sanwo-Olu.
A wani labarin kuma, Ranar Samun ‘Yancin Kai: Gwamna Akeredolu Ya Saki Fursunoni 16 Daga Gidan Yari
Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, a ranar Asabar, ya saki fursunoni 16 daga gidan yari na kasa dake Ondo.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mai shari’a na jihar, kuma kwamishinan shari’a, wanda kuma shi ne shugaban majalisar ba da shawara ta jihar kan jinkai, Mista Charles Titiloye.