Gwamna Ganduje, Da Sarkin Kano, sun yi musayar gaishe-gaishe, a lokacin da Sarkin na Kano, ya taya Gwamna Ganduje murna a kan sake zabensa da aka yi a karo na biyu.
Daga Abba Anwar
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya yi musayar gaisuwar Sallah tare da Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, a Abuja, a daren Juma’ar nan da ta gabata.
Shugabannin biyu sun gana, sun kuma taya juna murna a kan samun nasarar kammala azumin watan Ramadhan da kuma bukukuwan Sallah.
Dukkanin shugabannin sun yi kira ga al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin koyi da abubuwan da suka koya a lokacin azumin na Ramadhan.
Sarki Sanusi, ya yi amfani da wannan damar wajen taya Gwamna Ganduje murna a kan nasarar da ya samu na sake cin zaben gwamna a karo na biyu. Ya kuma yi wa Gwamnan fatan samun nasara a mulkin na shi na tsakanin 2019 zuwa 2023.
Domin neman samun kyakkyawar dangantaka a tsakanin hukumomin biyu na Jihar ta Kano, tattaunawar a tsakanin su za ta ci gaba.
Hamshakin mai kudin nan ne kuma dan kasuwa haifaffen Kano, Aliko Dangote da kuma shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya, Dakta Kayode Fayemi. Suka shirya taron sasantawan, ba wai shugaba Buhari ne ba, kamar yanda wani sashen manema labarai suke ta faman yadawa.
Anwar shi ne babban Sakataren yada labarai na Gwamnan Jihar Kano.