A ranar Litinin ne aka ayyana tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Hassan Dankwambo a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP mai wakiltar mazabar Gombe ta Arewa a zaben shekarar 2023.
An ayyana shi ne a matsayin wanda ya lashe zaben bayan wasu ‘yan takara biyu, Sanata Usman Bayero Nafada da Abdulkadir Hamma Saleh sun janye daga takarar, ta hanyar wata wasikar tabbatar da da wakilansu suka gabatar a wurin zaben.
Dankwambo ya kasance dan takarar jam’iyyar PDP a zaben 2019, amma dan takarar jam’iyyar APC, Sanata Saidu Ahmed Alkali ya doke shi a zaben.
A bangaren Gombe ta tsakiya, Alhaji Abubakar Aliyu, dan takarar gwamna na jam’iyyar CPC a shekarar 2011, ya samu kuri’u 59 inda ya kayar da Muhammadu Aliyu Baba wanda ya samu kuri’u uku, inda aka bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben kuma dan takarar PDP a Zabe Mai zuwa
A yayin da yake wakiltar mazabar Gombe ta Kudu, Mista Anthony Siyako Yaro ya samu kuri’u 59 a fafatawar da ya yi da Hajiya Fatima Binta Bello wadda ta samu kuri’u 57.
Binta Bello, wadda tsohuwar ‘yar majalisar wakilai ce, ita ce ‘yar takarar jam’iyyar a 2019, amma ta sha kaye a babban zaben da aka gudanar a hannun Kanar Bulus K. Amos (mai ritaya) na jam’iyyar APC.