Sanata Rochas Okorocha ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar (APC).
Tsohon gwamnan na jihar Imo ya bayyana hakan ne a wata wasika da ya aikewa shugaban majalisar dattawa wadda Ahmad Lawan ya karanta a zauren majalisar a ranar Laraba.
Okorocha ya ce zai yi jawabi ga taron manema labarai na duniya a ranar Litinin 31 ga watan Janairu 2022 domin bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a hukumance.