Sanatan Kaduna ta tsakiya wanda shi ne dan takarar gwamnan a jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya taya murna ga wadanda suka rabauta da tallafin karatu.
Uba Sani wanda ya raba tallafin ga wasu Dalibai a jihar ya bukace su da su zage damtse wajen yin karatu don amfanar da al’ummarsu.
KU KARANTA KUMA Zaman Lafiya Yana Da Matukar Muhimmanci Yayin Da Zabe Yake Karatowa – Dan Takarar Gwamna
Sanatan bayan bada tallafin ya kuma bayar da tallafin Naira miliyan 13,000000 lakadan ga wasu kungiyoyi hudu a ranar Asabar din nan.
Wannan na kunshe cikin sanarwar da ya aikewa jaridar DIMOKURADIYYA a yammacin ranar Asabar.
A kasa ga wasu hutuna
A Wani Labarin Kuma 2023: Zan Rage Rashin Aiki Da Kashi 50 A Shekara Ta Farko — Kola Abiola
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PRP, Kola Abiola ya ce idan aka zabe shi a zaben 2023, zai rage rabin yawan marasa aikin yi a kasar nan.
Alkaluman baya-bayan nan da Hukumar kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar ya nuna cewa rashin aikin yi a Najeriya ya kai kashi 33.3 bisa dari a rubu’i na hudu na shekarar 2020.