Shugabannin Kabilar Igbo dake jihar Kaduna sun tabbatarwa da dan takarar gwamnan jihar karkashin jam’iyyar APC Sanata Uba Sani goyon bayansu gare shi dari bisa dari.
Sun bayar da wannan tabbaci ne a Lokacin da Sanata Uba Sani ya kai musu ziyarar ban girma ga Shugaban su.
Jaridar Dimokuraɗiyya ta rawaito cewa wannan batu na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sanatan ya fitar a shafinsa na Facebook, ya na mai cewa ”Al’ummar Igbo dake jihar Kaduna sun Bani kwarin gwiwa.”
”Sun amince da takarar gwamnan jihar Kaduna da nakeyi kuma sunce za su tashi tsaye domin ganin hakar mu ta cimma ruwa.”
An bayyana hakan ne a lokacin da na kai ziyarar ban girma ga Babban Shugaban ‘yan kabilar Igbo, kakanmu, Ozo Cif Francis Nnaegbuna, Ozó Ndigbo da wakilan al’ummar yankin karkashin jagorancin shugaban su, Cif Francis Ani.
Babban majiɓinci, ma’ajin ilimi wanda ya ba da gudunmawa mai yawa ga ci gaban jihar Kaduna ya ba mu labarin daɗaɗɗiyar dangantakarsa da Marigayi Sardaunan Sakkwato, Sir Ahmadu Bello da wasu da dama daga Arewa.
”Bayan haka ne ya yi addu’ar Allah Ya ba ni nasara a zabe mai zuwa, ya kuma bukaci daukacin al’ummar Ibo da su goyi bayan takara ta.”
Al’ummar Igbo sun bayyana shirin su na kasancewa cikin harkokin siyasa a jihar Kaduna.
Sun shirya tsaf don kara kaimi a fagen siyasar jihar Kaduna, kamar yadda suka jajirce wajen saka hannun jari a sassa masu muhimmanci a jihar.
Jihar Kaduna dai gida ce ga ‘yan kabilar Igbo kuma duk da kalubalen da suke fuskanta na imanin da suke da shi a kan manyan abubuwan da jihar ke da shi har yanzu bai girgiza ba.
”Ci gaba da goyon bayan da al’ummomi daban-daban da masu ruwa da tsaki suka yi a kan takarata ta gwamna ya nuna karara cewa jihar Kaduna babbar tunga ce ta jam’iyyar APC.”
”Ba za mu taba daukar amanar mutane da wasa ba, domin kuwa Amincewarsu babban kalubale ce a gare mu.”
”Za mu tabbatar da cewa mun biya wannan amana ta hanyar tuntuɓar ƙalubalen ci gabanmu da kuma ƙarfafa imanin jama’a ga tsarin dimokuradiyya.”
”Ina godiya ga al’ummar Igbo mazauna jihar Kaduna da suka same ni na cancanci wannan karramawa da girmamawa Mutane ne na musamman; masu ƙwazo, masu aiki tuƙuru da wadata.”
”Sun bayar da gudunmawa mara misaltuwa wajen ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar Kaduna musamman ma Najeriya baki daya. Idan aka ba wa al’umma wa’adin mulki a 2023, zan tafiyar da gwamnati mai hade da jama’a, inda kowane dan kasa ba tare da la’akari da kabila da addini yake tafiyar da harkokin ci gaban kasarmu mai albarka ba.”
”A matsayina na Gwamna zan ci gaba da hulda da al’ummar Igbo kamar yadda na saba tun kafin in zama Sanata.”
Sanata Uba Sani Wanda ya Shahara wajen taimakon Al’umma yanzu Haka Yana cigaba da samun nasara a kokarinsa na Zama Gwamnan jihar Kaduna karkashin jam’iyar APC a zaben 2023 Mai zuwa.