Sanata Uba Sani ya taya Al’ummar Musulmi murnar shaida Babbar Sallah ta bana
Sanata Uba Sani Mai Wakiltar Kaduna ta Tsakiya, kuma Ɗan Takarar Gwamnan Jahar Kaduna a Jam’iyyar APC, ya Taya Al’ummar Musulmi murnar zagayowar Babbar Sallah ta bana.
Sanata Uba sani ya bayyana hakan ne a wani sakon sa na murnar bukin babbar Sallah “Happy Eid-al-Adha” daya fitar a shafin sa, zuwa ga ‘yan uwa Musulmin Najeriya da ma duniya baki daya.
KARANTA WANNAN LABARIN:Ƴan bindiga sun fi ƙarfin Jami’an tsaro, suna kashe su kamar Kaji a Zamfara — Inji Mazauna Jahar
Ya rubuta “Muna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki daya sanya mu cikin wannan biki na musamman. Idin layya biki ne na musamman da ke tunatar da mu cewa hakuri da amana da imani da biyayya da sadaukarwa da samun albarka mai yawa daga Allah.
“Hakuri da
sadaukarwa don kyakkyawar manufa ko gaskiya suma sune tushen ci gaba, gina al’ummomi masu zaman lafiya da kuma rayuwar bil’adama Kasancewa a nesa-nesa yana ƙara dagula yanayi kuma yana zurfafa tunanin rashin taimako da rashin ƙaunar juna.” inji Uba Sani
Ya ƙara dacewa “Mun kasance muna cikin rikici mai raɗaɗi da ƙalubale waɗanda ke gwada nufin ɗan adam. Amma har yanzu muna tafiya tare muna sa bege da rai da kuma amfani da damar da ake da su don inganta rayuwarmu”
” Lallai mu mutane ne masu juriya da karfi. Gwamnatoci a matakai daban-daban sun yi ta ƙoƙarin magance matsalolin tattalin arziki da tsaro amma har yanzu akwai bukatar a cigaba” Cewar Sanata Uba Sani.
Har ila yau a saƙon daya fitar yace “Ina jinjina wa ƴan Najeriya bisa haƙuri da sadaukarwar da suke yi na kwaikwayon hadayar Annabi Ibrahim domin biyayya ga Allah. Kuma saboda hakurin sa da sadaukarwa, Annabi Ibrahim ya sami lada mai yawa.
“Ina ce wa al’ummarmu a yau, hakuri da sadaukarwar da kuka yi a cikin wadannan yanayi musamman mawuyaci, tabbas ba zasu tafi a banza ba ko kuma ayi watsi da su a wajen Allah Madaukakin Sarki mai rahama ba. Shi ne zai kawar mana da Wadannan matsaloli, ya maido mana da zaman lafiya da ci gaban ƙasar mu”
Sanatan ya kuma bayyana cewa, Al’ummar Jahar Kaduna tuni suka san cewa ya gabatar da kansa domin Neman Gwamnan Jihar Kaduna, yana mai kira a garesu dasu taya shi da Addu’a domin samun nasara.
” Ina so in yi wa jama’armu hidima kuma in kai jihar zuwa ga tudun mun tsira. Ina neman goyon bayan dukkan maza da mata masu aminci. Mu yi aiki tare don isar da ayyuka yadda ya kamata ga jama’armu da kuma kare rayuwar su da dukiyar su wanda Wajibi ne a kan jihar mu da al’ummar mu. inji Sanata Uba sani.