Kotun daukaka kara a Kano ta soke takarar Sanata Danburam Nuhu da jam’iyyar PDP ta yi a matsayin dan takarar Sanata a Kano ta tsakiya.
A don haka ne, kotun ta amince da zaɓen fidda-gwani da jam’iyyar ta gudanar, ƙarƙashin shugabancin Shehu Wada Sagagi, wanda ya fitar da Laila Buhari a matsayin ƴar takara.
KU KARANTA: Yakin Neman Zabe: Atiku Da Tinubu Sun Yi Sabbin Naɗe Naɗe
A ranar 26 ga watan Satumba ne wata babbar kotun tarayya da ke Kano ta yi watsi da karar saboda rashin hurumin shari’a, bisa hujjar cewa an shigar da karar ne a Kano maimakon Abuja, sabanin tsarin majalisar shari’a ta kasa NJC kan al’amuran da suka shafi kararraaki kafin zaɓe.
Amma a hukuncin da mai shari’a Ita Mbaba ya yanke a jiya Laraba, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun ta yanke, inda ta ce ta yi kuskure wajen yin watsi da karar a kan wannan batu.
A yayin da take sauraren wata babbar hujja kan cancantarta kamar yadda aka shigar da ita ta hanyar sammaci, kotun ta ce a wani batu na gabanin zabe, za a yi amfani da hukuncin babbar kotun tarayya da kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya (1999) da aka yi wa kwaskwarima akan manufofin NJC, wanda karamar kotu ta dogara da shi.
Kotun ta umarci INEC da ta cire sunan Damburam tare da maye gurbinsa da na sunan Laila Buhari.
A wani labarin kuma: Peter Obi Bai Kai Darajar Kobo 10 Ba – Gwamna Sule
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya yi watsi da kididdigar yanar gizo da ta sanya Peter Obi, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour a gaban Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da kuma dan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar.
Sule ya yi ikirarin cewa sukar Obi, wanda tsohon gwamnan jihar Anambra ne, da gwamna mai ci, Charles Soludo ya yi, wanda ya rage darajar Obi a matsayin dan takarar shugaban kasa da kasa da kobo 10.