By Abbas Yakubu Yaura
Gagarumin ayyukan samar da ababen more rayuwa da gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya yi za su kara habaka tattalin arzikin jihar da rikicin Boko Haram ya daidaita na tsawon shekaru goma, mai ba da shawara kan gudanar da ayyuka, Engr. Yusuf Bello, ya ce.
DUBA WANNAN LABARIN: Taron APC: Jerin Sunayen Mutanen Buhari Da Gwamnoni Suka Kora
Engr Bello, babban abokin hadin gwiwa a kungiyar kula da ayyuka ta Samab International Links Limited, ya bayyana hakan a wata zantawa da yayi da manema labarai a ofishinsa dake Abuja.
Ya ce abin farin ciki ne cewa duk da kalubalen tsaro, Zulum yana mayar da jihar a matsayin abin koyi ta fuskar samar da ababen more rayuwa na jama’a da gudanar da mulki.
Bello ya ce, “Gwamna Zulum ya mayar da jihar da rikicin ‘yan tada kayar baya ya daidaita tsawon shekaru goma zuwa wurin gine-gine.
“Babu wani fannin da aka bari a baya. Yana gina gine-ginen da za su iya yin gasa a ko’ina a duniya ta fuskar inganci, aiki, farin ciki da kuma tasiri ga jama’a.”
Masanin kula da ayyukan ya ce Tigers na Asiya da na Gabas ta Tsakiya sun zama cibiyoyi na kasa da kasa “saboda juyin juya halin da shugabanninsu suka yi a shekarun baya. Abin da Farfesa Zulum ke yi ke nan a jihar Borno a halin yanzu.”
Ya ce Najeriya na fama da tabarbarewar ababen more rayuwa wanda a cewarsa hakan na matukar shafar yadda take samun karfin tattalin arzikinta. Ya ce dole ne gwamnatoci a dukkan matakai su sanya hannun jari wajen samar da ingantattun ababen more rayuwa domin habaka ci gaba.
Comments 1