Kwamitin da gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya kafa, a ranar Juma’a ya mika rahotonsa, inda ya zargi wadansu manyan sojoji da Sarakunan gargajiya da hannu wajen hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa a jihar Zamfara.
An kafa Kwamitin ne a watan Yuli, wanda tsohon Sufeto Janar na ‘yan Sandan Nijeriya, Muhammad Abubakar ya jagoranta. Inda aka dora masa alhakin bankado hanyoyin da za su magance matsalar tsaro a jihar.
Rahoton Kwamitin ya ba da shawarar korar wadansu jami’an soja tare da tumbuke wadansu Sarakunan gargajiya.
Muhammad Abubakar ya shaidawa gwamnan cewa; akwai bukatar a tumbuke Sarakuna 5 tare da Hakimai 33 da wadansu masu Unguwanni wadanda ake da tabbacin suna da hannu wajen ayyukan ‘yan bindiga a jihar har na tsawon shekara 10.
Har wala yau Kwamitin ya zargi sojoji har guda 10 wadanda suka kai matakin Ofisoshi tare da wadansu jami’an ‘yan sanda da wadansu fararen hula da suke goyon bayan ‘yan bindigar wadanda suka kashe daruruwan al’ummar da ba su ji ba su gani ba. Tare da kona kauyuka da kuma tarwatsa gonaki da abinci da kuma kiwo.
Da yake maida jawabi, gwamnan ya yiwa Kwamitin alkawarin tabbatar da shawarar da suka bayar ba tare da yi wa wani wata alfarma ko tsoron wani ba. Gwamnan ya ce ba zai yadda wata alaka ta addini ko ta kabilanci ko ta jini ko ta yanki ta hana shi daukar matakan da suka dace ba.
Sannan ya ce; wadanda kuma gwamnatin jihar ba za ta iya hukuntawa ba saboda a dokance gwamnatin jiha ba ta da ikon haka, to za su mika su zuwa ga gwamnatin tarayya domin a hukunta su.
Da aka tuntubi Kakakin rundunar Atisayen Hadarin Daji A Zamfara, wato Oni Orisan, ya ce ba zai ce komai ba dangane da rahoton, saboda bai samu wani bayani ba.