Sarakunan arewacin ƙasar nan sun gudanar taro kan rikice-rikce dake faruwa a faɗin arewacin Najeriya.
Taron da aka gudanar a Kaduna ƙarkashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, na ƙoƙari ne wajen lalubo mafita ga ƙaruwar matsalar tsaro da ke addabar yankin da ma faɗin Najeriya.
Sarakunan sun kuma tattauna kan irin tasirin da illar da Koroma ta yi wa rayuwar jama’a, da nufin bayar da shawarwari kan yadda za yi wa tufkar hanci.
Idan ba a manta ba, a makonnin bayan, Sarkin Musulmi ya ziyarci gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, inda suka tattauna akan batun tsaro a jihar da sauran al’amura.
Bayan ganawarsu, El-Rufai ya shaidawa manema labarai cewa sarkin Musulmi ya ba shi shawarwari kan hanyoyin shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar, musamman ganin yadda rikicin ƙabilanci a kudancin Kaduna ke damun mutane a faɗin Najeriya.
Yankin arewacin Najeriya na fama da matsalolin tsaro da suka haɗa da na ƙungiyar Boko Haram da ake faman yaƙi da ita tun a shekarar 2009.
A wani cigaban sojoji sun sanar da tarwatsa masana’artar makamai tare da kama ɗaruruwan iyalan ‘yan ƙungiyar Darul Salam a jiharihar Nasarawa, lamarin da masana ke cewa wata barazanar tsaro ce da ke buƙatar a sa ido sosai a kai.
Ayyukan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane musamman a arewa masu-gabas da arewa ta tsakiya na cikin manyan matsalolin yankin, inda rikicin manoma da makiyaya ya zama tamkar ruwar dare.